Yan Daba Ɗauke da Makamai Sun Kai Hari Wurin Gangamin Taron Atiku a Kaduna

Kaduna – Rahoton da muke samu ya nuna cewa wasu yan Daba sun faramki magoya bayan PDP a Ranches Bees Stadium, Kaduna, wurin gangamin taron ɗan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasan ya tabbatar da faruwar lamarin a wani rubutu da ya saki a shafinsa na dandalin Facebook ranar Litinin.

Atiku ya yi kira ga shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, da ya umarci sauran jam’iyyu su dakatar da mambobinsu daga yunkurin ta da yamutsi a wurin taron.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments