• About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
No Result
View All Result
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
Home politics

Mahimman batutuwa da dan takarar shugabancin kasa a jam’iyyar PDP ya bayyana a ranar laraba

B. IMAM by B. IMAM
September 29, 2022
in politics
0
0
SHARES
Share on FacebookShare on Twitter

Bayan shafe tsawon lokaci ana dakon zuwan wannan rana, jam’iyyun siyasa a Najeriya sun fara yawon neman ƙuri’un masu zaɓe a hukumance.

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP ba ta yi ƙasa a gwiwa ba, inda ta ƙaddamar da tawagar kamfe ɗinta na takarar shugaban ƙasa a ɗakin taro na International Conference Centre da ke Abuja ranar Laraba.

RelatedPosts

NNPC affirms to reclaim its mandate Despite That INEC mentioned Shekaru as winner.

NNPC affirms to reclaim its mandate Despite That INEC mentioned Shekaru as winner.

February 28, 2023
Election: INEC releases results of 38 LGAs in kano

Election: INEC releases results of 38 LGAs in kano

February 27, 2023

No team to turn Nigeria around” than my husband and Datti: Obi’s wife

January 4, 2023

Ɗan takarar shugabancin kasar Atiku Abubakar da mataimakin sa, Ifeanyi Okowa, da sauran jiga-jigai na cikin waɗanda suka yi jawabai a wurin taron.

“yawancin mutanen da suka taru a nan ƙwararrun ‘yan siyasa ne irina waɗanda siyasa ke gudana a cikin jininsu saboda ƙaunar da suke yi wa mutane da kuma ƙasarsu,” a cewar Atiku.

Duk da cewa babban abin da ya tara su shi ne ƙaddamar da tawagar kamfe, an kuma ƙaddamar da wani littafi da aka rubuta game da hukunce-hukuncen da kotuna suka bayar game da ƙararrakin da Atiku ya shigar a tsawon shekaru mai suna ‘Landmark Constitutional Law Cases in Nigeria; The Atiku Abubakar Cases’.

Sai dai ba a ga Gwamnan Rivers Nyesom Wike ba a wurin taron sakamakon rikicin da ke ci gaba ɗaukar sabon salo tsakaninsa da ɓangaren Atiku. Kazalika, tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan bai halarci taron ba.

Sauran waɗanda suka yi jawabai sun hadar da shugaban tawagar kamfe na Atiku, Gwamna Aminu Tambuwal na Sokoto, da muƙaddashin shugaban PDP, Iliya Damagum, da Sanata Dino Melaye.

An ƙaddamar da littafi kan rayuwar Atiku yayin taron

Ga abu biyar da Atiku ya faɗa yayin jawabin nasa.

‘Taron yau ba na gama-gari ba ne’
Ɗan takarar shugaban ƙasar ya fara jawabinsa da godiya ga jagororin kamfe ɗin, yana mai bayyana su da “masu kishin ƙasa da son al’ummarsu”.

Atiku ya ce muhimmancin taron ne ya sa ba zai wuce shi ba “saboda taron na yau ba gama-gari ba ne”.

A cewarsa: “Yau ba rana ce kamar sauran ranaku. Ƙaddamar da tawagar kamfe ta shugaban ƙasa ba taron gama-gari ba ne. Samsam ba haka ba ne.”

Me zai faru idan ba a warware rikicin APC da PDP nan kusa ba?
22 Satumba 2022
Ba za mu iya aiwatar da buƙatun Nyesom Wike ba – Jam’iyyar PDP
11 Satumba 2022
Ba zan sauka daga shugabancin PDP ba – Iyorchia Ayu
31 Agusta 2022
‘Najeriya ta ɓalɓalce a ƙarƙashin mulkin APC’
Kamar yadda aka saba, duk lokacin da jam’iyyun adawa suka samu dama kan soki APC mai mulki, kamar yadda ita ma take kan soki mai adawa da ita.

A wannan karon, Atiku ya yi iƙirarin cewa Najeriya ta shiga “halin rashin tsari” a ƙarƙashin mulkin APC na shekara bakwai bisa jagorancin Shugaba Muhammadu Buhari, wadda ta hau mulki a 2015.

“Ƙasarmu ta afka cikin rashin doka da oda. Wannan gwamnatin ta gaza wajen aiwatar da ƙashin bayan abin da aka zaɓe ta a kai; kare rayuka da dukiyoyi,” a cewarsa.

“Kowa ya san haka. Tattalin arzikinmu ya wargaje. Mutanenmu na fuskatar matsin rayuwa a kullum.

“Rashin haɗin kan da muke fama da shi a yanzu ya zarce na lokacin yaƙin basasa. An wargaza zumuncin da ya haɗe kanmu ta hanyar nuna wariya da rashin amincewa da juna.”

‘Tsarin gwamnati yanzu ba na adalci ba ne’
Da yake ci gaba da kokawa kan matsalolin da ya zargi gwamnatin APC da jefa ƙasa, Atiku ya ce tsarin gwamnati a yanzu ya zama “mara adalci”

“Tsarin gwamnati a yanzu cike yake da rashin adalci ta hanyar fifita gwamnatin tarayya da kuma zalintar sauran gwamnatoci, abin da ya zama wata hanya ta jawo rashin ci gaba da kuma cin hanci.

“Irin wannan tsarin bai dace da ƙarni na 21 ba, wanda ake buƙatar ya kusanto da haɓakar tattalin arziki kusa da al’ummarmu.”

‘Muna da tsarin gyara Najeriya’
Bayan lissafo abubuwan da ya bayyana a matsayin matsala, Atiku ya ce jam’iyyarsu ta PDP na da tsarin ceto Najeriya daga ƙangin da take ciki.

“Shirinmu game da Najeriya shi ne ceto ta ta hanyar adalci da daidaito da haɗin gwiwa tsakanin al’ummominmu mabambanta.

“Na biyu shi ne kafa gwamnatin dimokuraɗiyya wadda za ta saka karewa da kuma inganta rayuwar mutane a gaba.

“Na uku, gina tattalin arziki mai ƙarfi da zai samar da dama ga mutane da ƙasa baki ɗaya, sannan ya fitar da miliyoyi daga ƙangin talauci.

“Za mu kafa cikakkiyar gwamnatin tarayya da za ta bai wa kowane mataki na gwamnati dama da wakilci da za su ba da damar kare iyakokinmu da tsaron ƙasa da kuma haɗin kai.”

‘Mun taru ne don ceto Najeriya’
Har yanzu dai game da taron, Atiku ya bayyana cewa ba su taru kawai don ƙaddamar da tawagar kamfe ba, sun taru ne don ceto Najeriya.

“Mene ne abin da ya tara mu a nan? Mene ne aikinmu? Ba mu taru a nan kawai don mu ƙaddamar da tawagar kamfe ba. A’a, ya wuce haka.

“Aikinmu shi ne haɗa kai don ceto ƙasarmu mai albarka. Wannan shi ne babban muradinmu.

“Amma abin da za mu fara yi shi ne ƙwace mulki daga hannun jam’iyyar da ta jefa mu cikin wannan matsalar. Don aiwatar da hakan, dole ne mu haɗa kai mu cinye zaɓukan da ake shirin gudanarwa a shekara mai zuwa.”

ShareTweetSendSharePin
Previous Post

Rahoto akan Dalilin da ya sa darajar dala ke hauhawa

Next Post

Daga hukumar EFCC guda daga cikin gwamnonin arewa ya amsa kira

B. IMAM

B. IMAM

RelatedPosts

NNPC affirms to reclaim its mandate Despite That INEC mentioned Shekaru as winner.
politics

NNPC affirms to reclaim its mandate Despite That INEC mentioned Shekaru as winner.

by Aksam Media
February 28, 2023
0

WThe New Nigeria Peoples Party (NNPP) Kano State vowed to reclaim its mandate in the just-concluded Kano Central Senatorial election....

Read more
Election: INEC releases results of 38 LGAs in kano

Election: INEC releases results of 38 LGAs in kano

February 27, 2023
No team to turn Nigeria around” than my husband and Datti: Obi’s wife

No team to turn Nigeria around” than my husband and Datti: Obi’s wife

January 4, 2023
Gawuna plans a lot for the development of youths: Muhammad Garba

My administration will not disappoint peoples of Kano state : Gawuna

December 20, 2022
Gawuna plans a lot for the development of youths: Muhammad Garba

Gawuna plans a lot for the development of youths: Muhammad Garba

December 12, 2022
Parties speak for the new cash withdrawal limits

Parties speak for the new cash withdrawal limits

December 12, 2022
0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Login
Notify of
guest
guest
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments
  • Trending
  • Comments
  • Latest
Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

March 10, 2023
Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

February 21, 2023
Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

February 11, 2023
INEC tayi umarnin kara gudanar da zabe a jihar Kogi

Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

March 19, 2023
CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

2
Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

1
Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

1
Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

1
China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO

China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO

March 25, 2023
Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu

Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu

March 25, 2023
APC ta musanta ganawa tsakanin Tinibu da alkalin alkalai na kasa

APC ta musanta ganawa tsakanin Tinibu da alkalin alkalai na kasa

March 24, 2023
CBN ya soma gudanar da rangadi domin hukunta Bankuna da basa bayar da tsofaffin takardun kuɗi ga alumma

CBN ya soma gudanar da rangadi domin hukunta Bankuna da basa bayar da tsofaffin takardun kuɗi ga alumma

March 24, 2023
  • Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yanzu-yanzu an kama wani Dan Majalisa dauke da makuden kudaden waje

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO
HAUSA NEWS

China ta soki kasar Amurka bayan da ta shiga UNESCO

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta ce kafin Amurka ta koma cikin hukumar raya ...

March 25, 2023
Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu
HAUSA NEWS

Ada na sha ruwan kwata sabo da Buhari da jam’iyar sa amma yanzu Ina Allah wadai da ita: Matashi Aliyu

Aliyu Muhammad ya tsallake rijiya da baya a 2019, saboda makauniyar soyayya daya samu kansa a ciki ta Shugaba Muhammadu ...

March 25, 2023
APC ta musanta ganawa tsakanin Tinibu da alkalin alkalai na kasa
HAUSA NEWS

APC ta musanta ganawa tsakanin Tinibu da alkalin alkalai na kasa

Kwamatin yakin neman zaben na Dan takarar jam’iyar APC Asiwaju Bola Ahmed Tinibu ya musanta raderadin da wasu kafafen sadarwa ...

March 24, 2023
CBN ya soma gudanar da rangadi domin hukunta Bankuna da basa bayar da tsofaffin takardun kuɗi ga alumma
HAUSA NEWS

CBN ya soma gudanar da rangadi domin hukunta Bankuna da basa bayar da tsofaffin takardun kuɗi ga alumma

Daga kabiru A Dukawa Babban bankin Najeriya CBN ya ci alwashin hukunta duk wani bankin yan kasuwa da ya samu ...

March 24, 2023
Matashi mai tattaki daga Garin Kubau zuwa Kaduna dan taya murna ga,  sen Uba Sani, tafiya ta nisa
HAUSA NEWS

Matashi mai tattaki daga Garin Kubau zuwa Kaduna dan taya murna ga, sen Uba Sani, tafiya ta nisa

Matashi mai suna Yusuf Umar ya ga dacewar zuwa Kaduna garin gwamna ne domin taya sabon zababben gwamnan jihar Kaduna ...

March 24, 2023

Recent Comments

  • Ibrahim S kabara on Hukumar kula da ayyukan yan sanda ta raba lambobin kiran waya Dan sa Ido a ayyukan yan sanda a lokacin zabe
  • Abbas Jibril on Katu ta Yankewa AbdulJabbar Kabara Hukuncin Kisa ta hanyar Rataya
  • Walid Y Haris on Akwai Malaman cocin dake kallan batsa a yanar gizo ta wayoyinsu-Fafaroma
  • Abba Garba Sufi on Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.
  • Sani saadu aliyu on CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

No Result
View All Result
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

wpDiscuz