Kotu ta wanke dantakar babbar jam’iyar adawa na kasar Saliyo

Babban abokin hamayyar shugaban kasar Saliyo mai barin gado a zabe mai zuwa, ya kawar da wata babbar matsala da ka iya hana shi tsayawa takara.

Samura Kamara, wanda Julius Maada Bio ya doke shi a zaben 2018, yana fuskantar shari’a tun watan Fabrairu bisa zargin cin hanci da rashawa.

Magoya bayansa wadanda suka ce lamarin na da nasaba da siyasa, suna fargabar za a yanke masa hukuncin gaggawa wanda zai hana shi shiga zaben da za a yi ranar 24 ga watan Yuni.

Sai dai mai magana da yawun hukumar zaben ya ce, Kamara ya gabatar da bukatarsa na yin takara a hukumance a ranar Litinin, matakin da ya biyo bayan umarnin dage ci gaba da shari’ar tasa har zuwa ranar 14 ga watan Yuli.

A gefe guda kuma, wata babbar kotu a jiya Talata ta ba da umarnin a saki fasfo din Kamara, wanda zai ba shi damar halartar taron kungiyar Commonwealth a Biritaniya, kamar yadda kakakin sashin shari’a Elkass Sannoh ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments