• About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
No Result
View All Result
AKSAM MEDIA
No Result
View All Result
Home HAUSA NEWS

Faduwar fan din ingila ya daga darajar kudaden afuruka

B. IMAM by B. IMAM
September 27, 2022
in HAUSA NEWS
0
0
SHARES
Share on FacebookShare on Twitter

Darajar cedi din Ghana na daga cikin kudaden kasashen Afurka da suka fadi

Mintuna 24 da suka wuce
A daidai lokacin da darajar Fan din Ingila ta karye, su kuwa kudaden wasu kasashen Afirka tagomashi suka samu, inda darajarsu ta dan farfado.

RelatedPosts

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

March 21, 2023
Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

March 21, 2023

An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

March 21, 2023

A ranar Litinin, darajar fan din ta fadi da kashi 4, idan aka kwatanta da dalar Amurka a kasuwannin Asiya, darajar Shilling din Kenya ya farfado da 0.15, kan fan guda.

A dayan bangaren kuma, an dara a wasu kasashen Afirka, inda darajar kudin Zambia kwacha, da pula na Botswana, da cefar kasashen Afurka su ma sun samu tagomashi.

Sai dai, darajar kudaden Afirka ta Kudu rand, da naira ta Najeriya lamarin ba mai dadi ba ne, saboda sun kara faduwa kasa warwas.

Wannan rana na zuwa ne daidai lokacin da wasu kasashen Afirka suka fuskanci asarar faduwar darajar kudaden idan aka kwatanta da dalar Amurka da fan din Ingila.

Cedin Ghana shi ya fi kowanne karyewa, ya yi faduwar da ba a a taba gani ba cikin shekaru da dama, tun farkon shekarar nan ta yi kasa da kashi 40 idan aka kwatanta da dalar Amurka.

Cedin ya kara yin kasa da kashi 20 kan fan din Ingila a dai wannan shekara da muke ciki. Amma cedi ya dan yi sama kadan da kashi 10.83 da safiyar ranar Litinin.

“Kasashe na fadi tashi kan farfado da tattalin arzikinsu, musamman ganin kayan da suke fitarwa sun ninka wadanda ke shiga kasashen,’’ in ji Richmond Frimpong, mai sharhi kan lamura a Ghana.

Wannan ya kara janyo bukatar kudaden kasashen waje, da tashin tsadar kayayyaki.

Me ya janyo faduwar darajar fan?
Darajar fan din Ingilar ta fadi a kasuwar duniya, daidai lokacin da gwamnati ta sanar da Karin kudin haraji da ba a taba gani ba cikin shekaru 50.

Fan ya fadi da kusan kashi 1.03 da safiyar Litinin, amma ya dan dago kafin faduwar rana da kashi 1.08.

Sakataren baitil malin Birtaniya, Kwasi Kwarteng ya yi alkawarin rage haraji kari akan fan biliyan 45 da ya sanar a ranar Juma’a.

Masu zuba hannun jari na kasashen Duniya, na saye da sayar da hajarsu da kudaden waje. Manufar ita ce samun riba, saboda za su sayi kudaden masu daraja.

Darajar fan din ta fadi saboda masu zuba jari na saída ita, saboda rashin tabbacin shirin gwamnatoci da ke nuku-nuku, In ji Jabe Foley na Rabobank.

“Sun damu matuka kan sanarwar gwamnati na rage kudin haraji kuma ba lallai su ba da cikakken tallafinsa ba,” in ji ta.

Wannan na daga cikin dalilan da ya tilastawa gwamnatoci cin bashi.

Hakan zai janyo cin bashin makudan kudade, a daidai lokacin da bankin Ingila zai fara saida wasu daga cikin basukan gwamnatin.

Darajar dalar Amurka da fan sun dan farfado a makwannin da suka gabata, to amma na dan lokaci baya sanar da kwarya-kwaryan kasafin kudi domin farfado da dala.

A farkon watan Satumba dalar ta fadi da kashi 1.35, karon farko da ta yi kasa da 1.14, cikin shekaru 40.

Hakan na faruwa sakamakon tashin farashin makamashi da sauran kayayyaki, da ke ci gaba da sanya tattalin arzikin duniya cikin garari.

An dade ba a ga tashin farashin kayan abinci cikin sauri ba cikin shekaru 40, farashin makamashi da fetur ma ba a cewa komai.

A bana, darajar fan karye fiye da dalar Amurka da sauran kudade.

Ita ce faduwa mafi muni cikin shekara da ka fuskanta tun bayan ficewar Birtaniya daga Tarayyar Turai a shekarar 2016.

Ana amfani da darajar kudi a kasuwar musayar kudade, ta hanyar saye da sayarwa.

Wasu abubuwan
Akwai kuma abubuwa da dama da suka hada da;

Tattalin arziki: Bunkasar tattalin arziki na sanya darajar kudin kasar ta samu tagomashi, saboda wasu kasashe za su zuba jari a ciki, za su bukaci kudin kasashen domin hakan, hakn zai sanya bukatar ta karu.

Adani: Idan bankin Ingila ya kara kudin ruwa, hakan zai ja hankalin masu zuba jari ko ajiyar kudade, su kara azamar bukatar fan din Ingila.

Farashi: Idan kayan da Birtaniya ke samarwa sukai arha fiye da na wasu kasashe, ‘yan kasuwa daga ketare za su bazama domin bukatar kudin fan domin saya. Wannan zai sanya darajar kudin ta karu

Harkokin kudin gwamnati: Halin da bankin gwamnati ke ciki, da abin da ke kasa, da bashin da ake bi, ka iya shafar darajar kudi.

Hasashe: Tsadar kudin, da saye da sayarwa da hasashen da ake yi watakil darajar ta karu, na sanya mutane hadamar saye domin cin riba nan gaba.

Abin lura shi ne, tsahon wane lokaci za a dauka darajar kudin na faduwa.

Tags: AIR FORCEALAN WAKAALJAZEERAAREWA24ASUUbanditBBCBOSHOTVBUK RADIOCNNCOMMDWFACEBOOKFIELDGARBA SHEHUGWANJAHAUSA7INIZZAR SOjambKADAURA24KAKAKILABARI NAMASSMC TAGWAYEMESSIMILITARYNASUNBCnewsOXPORTPREMIER RADIORARIYARIFSAFARA'UsportTAMBARIN HAUSATWEETAVISION RADIOvoaWHATAPP
ShareTweetSendSharePin
Previous Post

Poverty pushes Afghan children to work at brick kilns.

Next Post

Ba wani abun bauta sau Allah shanu sun nuna fishin su a zahiri a kasar indiya

B. IMAM

B. IMAM

RelatedPosts

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna
HAUSA NEWS

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

by Aksam Media
March 21, 2023
0

Rahotanni na nuni da cewa jam'iyun adawa da suka yi takarar gwamnan a jihar Kaduna sun yi watsi da sakamakon...

Read more
Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

March 21, 2023
An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

March 21, 2023
Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna

Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna

March 21, 2023
Ina Zargin Wasu Abokan Sana’armu ta Fim Da Hannu wajen kone gida na da na Rarara: Baba cinedu

Ina Zargin Wasu Abokan Sana’armu ta Fim Da Hannu wajen kone gida na da na Rarara: Baba cinedu

March 20, 2023
Yanzu-yanzu INEC ta sanar da Sanata  Uba Sani  a matsayin wanda ya ci zabe a jihar Kaduna

Yanzu-yanzu INEC ta sanar da Sanata Uba Sani a matsayin wanda ya ci zabe a jihar Kaduna

March 20, 2023
0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Login
Notify of
guest
guest
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments
  • Trending
  • Comments
  • Latest
Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

March 10, 2023
Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

February 21, 2023
Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

February 11, 2023
INEC tayi umarnin kara gudanar da zabe a jihar Kogi

Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

March 19, 2023
CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register

2
Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

Latest News On N-Power Stipends For Today September 5th, 2022.

1
Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

Masu tura finafinan Hausa sun koka da rashin samun tallafi daga gwamnati duda dinbin yawan da suke dashi

1
Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.

1
Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

March 21, 2023
Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

March 21, 2023
An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

March 21, 2023
Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna

Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna

March 21, 2023
  • Kamfanin MTN  ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    Kamfanin MTN ya canza hanyoyin saka Kati da siyan data da duba Balas

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yanzu-yanzu: INEC ta fitar da sabuwar Sanarwa

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yadda wata makaranta mai dauke da tarin marayu suka yi bikin saukar Al-qur’ani

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Sakamakon zabe na kananan hukumomi 34 na jihar Kano

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
  • Yanzu-yanzu an kama wani Dan Majalisa dauke da makuden kudaden waje

    0 shares
    Share 0 Tweet 0
Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna
HAUSA NEWS

Jam’iyun adawa sunyi watsi da sakamakon zaben jihar Kaduna

Rahotanni na nuni da cewa jam'iyun adawa da suka yi takarar gwamnan a jihar Kaduna sun yi watsi da sakamakon ...

March 21, 2023
Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina
HAUSA NEWS

Jam’iyar PDP tayi watsi da sakamakon zaben jihar katsina

Dan takarar gwamnan jihar katsina  na babbar jam'iyyar hamayya ta PDP, a zaben da ya gabata, Sanata Yakubu Lado Dan ...

March 21, 2023
An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna
HAUSA NEWS

An Sami mamakon ruwan sama karo na farko a bana a garin Kaduna

Daga Hassan Umar Gwammaja A dare jiya an samu mamakon ruwan sama mai karfi (Na farko a jihar Kaduna) wanda ...

March 21, 2023
Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna
HAUSA NEWS

Ganduje ya dage dokar hana fita da aka ayyana ta jiya kafin bayyana wanda ya lashe zaben gwamna

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cire dokar hana fita da ta kakabawa al'ummar jihar a jiya bayan ayyana Abba kabir ...

March 21, 2023
Ina Zargin Wasu Abokan Sana’armu ta Fim Da Hannu wajen kone gida na da na Rarara: Baba cinedu
HAUSA NEWS

Ina Zargin Wasu Abokan Sana’armu ta Fim Da Hannu wajen kone gida na da na Rarara: Baba cinedu

Shahararren jarumi kumaawaki a masana'antar Kannywood Baba Chinedu yace "An Sacè Mun Kaya Na Sama Da Milyan Gòma A Lokacin ...

March 20, 2023

Recent Comments

  • Ibrahim S kabara on Hukumar kula da ayyukan yan sanda ta raba lambobin kiran waya Dan sa Ido a ayyukan yan sanda a lokacin zabe
  • Abbas Jibril on Katu ta Yankewa AbdulJabbar Kabara Hukuncin Kisa ta hanyar Rataya
  • Walid Y Haris on Akwai Malaman cocin dake kallan batsa a yanar gizo ta wayoyinsu-Fafaroma
  • Abba Garba Sufi on Kungiyar masu hada-hadar wayoyin hanu ta jihar Kano ta shirya gasar kwallon kafa ga yayanta dake fadin jihar Kano.
  • Sani saadu aliyu on CBN za ta bayar da tallafi ga graduate ku shiga nan kuyi register
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

No Result
View All Result
  • About Us
  • Advertisiment
  • Contact Us
  • Home
  • Privacy Policy
  • Radio

© 2023 Aksam Meadia LLC

wpDiscuz