Kasar Saudiya ta magantu bisa kashe Ayman Azzawahiri da Amurka tayi

Ma’aikatar harkokin wajen Saudi Arabia ta yi maraba da kisan da Amurka ta yiwa shugaban kungiyar al-Qaeda Ayman al-Zawahiri, wanda hukumomi suka shafe tsawon lokaci suna nema ruwa a jallo sakamakon hannunsa a kitsa harin ranar 11 ga watan Satumban 2001 ko kuma 9/11.

Sanararwar ma’aikata harkokin wajen ta Saudiyya na zuwa ne jim kadan bayan sanarwar da shugaba Joe Biden na Amurka da ke ikirarin cewa a wani samame ne da ta kai da jirgi mara matuki, Amurka ta kashe Zawahiri, daya daga cikin ‘yan ta’addan da aka fi nema ruwa a jallo a duniya.

Shugaba Joe Biden a jawabinsa na asubahin yau talata ya ce Amurka ta yi nasarar kisan jagoran ne a hare-haren da hukumar CIA kai da jiragen yaki kan maboyar mayakan na al-Qaeda da ke birnin Kabul na Afghanistan.

A cewar Joe Biden a lahadin da ta gabata ne dakarun na ta suka kaddamar da farmakin a babban birnin na Afghanistan.

Zawahiri wanda kwararren Injiniya ne ya karbi jagorancin kungiyar al-Qaeda ne a shekarar 2011, bayan mutuwar Osama bin Laden, wanda aka yi amannar tare suka kitsa harin na ranar 11 ga watan Satumban 2001 ko kuma 9/11.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments