Wata kotu a Birtaniya ta samu ɗan majalisar dattawa, Ike Ekweremadu da matarsa da laifin yunkurin safarar sassan ɗan adam.
Shari’ar ta shafi dauko wani dan Najeriya mai shekaru 21 zuwa Birtaniya domin a cire ƙodarsa a bai wa diyar Ekweremadun.
Kotun ta kuma sami wani likita mai shekaru 50, Dr Obinna Obeta da haɗa baki da dan siyasar wajen samo mutumin saboda a cire masa koda.
Masu shigar da kara sun ce za a cire kodar mutumin ne domin a saka wa Sonia, ɗiyar Ekweremadu mai shekaru 25.
Kotun ta wanke Sonia da hannu a tuhumar da ake yi mata.