Jam’iyar PDP ta Fitar da kuɗin fom ɗin takarar shugaban kasa

Jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) mai samun goyon bayan Nyesom Wike ta fitar da jadawalin gudanar da zaɓe, tare da sanya kuɗin fam ɗin tsayawa takarar shugaban ƙasa a kan Naira miliyan 51.

A cikin jadawalin da jam’iyyar ta fitar, ta bayyana matakan da za a bi wajen zaɓen ‘yan takara a matakai daban-daban, ciki har da zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa.

Rahotanni sun nuna cewa matakin ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen babban zaɓen ƙasa mai zuwa, inda jam’iyyun siyasa ke ƙoƙarin tsara dabarun su domin samun nasara.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments