Wani matashi da ya kware wajan iya Damfara a Banki ya fada komar jamian tsaro

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa sun yi ram da wani matashi da ake zargi da zama ‘dan damfara a kan hanyarsa ta zuwa Yola

An kama matashin mai suna Joseph Nwakibe da katinan ATM guda 10 na bankuna daban-daban wadanda suke damfarar mutane da su

An gano cewa suna hawa layi kamar kwastomin bankin yayin da suke musayar kati ga wadanda suka nemi a taimake su sannan su hada da lambar katin don damfara

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta damke wani da ake zargi da zama ‘dan damfara mai suna Joseph Nwakibe wanda wani abokinsa mai suna Obinna Ajima ya gayyata a Yola domin aiwatar da lamurran ta’addanci.

An bayyana hakan ne a wata takarda da rundunar ‘yan sandan suka fitar a ranar Juma’a wacce kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Suleiman Yahaya.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments