ranar Litinin wasu daga cikin wakilan jam’iyyun na bangaren ‘yan adawa suka fice daga zauren tattara sakamakon zaben bayan da suka nuna rashin gamsuwar kan abin da ke faruwa.
Jamiâyyun PDP, LP da ADC, sun yi kira da a soke zaben shugaban kasar da aka yi, suna masu ikirarin an tafka magudi a zaben.
Shugabannin jamâiyyun sun bayyana hakan ne a wani taron manema labarai na hadin gwiwa da suka yi a Abuja a ranar Talata.
A cewar jamâiyyun, an hada baki da jamiâan hukumar ta INEC a rumfunan zabe wajen yin arangizon kuriâu ta hanyar sakamakon zaben a naâurar IReV da ake ganin sakamakon a yanar gizo.
Shugaban jamâiyyar PDP Iyochia Ayu da na LP, Julius Abure sai na ADC Ralph Nwosu, su ne suka bayanna wannan matsaya yayin taron manema labaran a a Abuja.
Abure, shi ne ya yi magana a madadin jamâiyyun uku.
Jamâiyyun sun kuma ce sun yanke kauna ga shugaban hukumar ta INEC Farfesa Mahmood Yakubu inda suka nemi da a nada wani wanda ba zai nuna son banbanci ba.
Shugabannin jamâiyyun sun yi zargin cewa rashin bayyana sakamakon zabe a akwatunan zabe ta shafin hukumar da aka tanadar don sanya sakamakon zabe wato IREV, shi ya tabbatar da cewa jamiâan hukumar INEC sun sauya sakamakon zaben shugaban kasa da na âyan majalisun tarayya da aka gudanar a ranar ta Asabar.
âBa a yi zabe da gaskiya ba balle ma a ce an yi adalciâ sannan ya kara da cewa, ana ci gaba da soke sakamakon zabe a yankuna inda jamâiyyun adawa suke da rinjayeâ. Abure ya ce.
A ranar Litinin wasu daga cikin wakilan jam’iyyun na bangaren ‘yan adawa suka fice daga zauren tattara sakamakon zaben bayan da suka nuna rashin gamsuwar kan abin da ke faruwa.
Sai dai ciki watan sanarwa da ta fitar a ranar Talata, INEC ta musanta zargin da jamâiyyun suka yi, tana mai cewa kiran da suke yi a sauke Farfesa Yakubu ba shi da tushe balle makama.
Babban Sakataren yada labaran hukumar ta INEC, Rotimi Oyekanmi, ya ce akwai kaâidoji da hanyoyi da aka shimfida wajen shigar da korafe-korafe yana mai cewa zarge-zargen da suka yi, babu hujj a ciki.