Nahiyar Afrika ta dauki hanyar zama cibiyar aiyukan taaddanci na Duniya: Macky Sall

Shugaban Kungiyar Tarayyar Afrika (AfB) kuna Shugaban kasar Senegal, Macky Sall ya bayyana nahiyar Afrika a matsayin yankin da ya fara zama cibiyar aiyukan taaddanci na Duniya.

Da yake jawabi a wajen taron tattauna wa bisa zaman lafiya da tsaro da aka gudanar a Dakar, babban birnin kasar Senegal, Sall ya ja hankali game da karuwar aiyukan ta’addanci a sassa daban-daban na nahiyar.

Da yake bayyana cewa ta’addanci ya zama matsala a duniya, Sall ya yi nuni da cewa Afrika ta biya babban farashi a wannan fanni.

Shugabannin kasashe, ministoci, jami’an diflomasiyya da wakilan kungiyoyin kasa da kasa da dama ne suka halarci taron na kwanaki biyu.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments