Alhaji Mustafa Ali Ya bayyana cewar yanzu haka wakilan kungiyarsu suna jihar Abiya don jin yadda lamarin yake tare da ganawa da gwamnati don biyan yan kasuwar su da lamarin ya rutsa da shanun su diyya.
Shugaban ya kuma bayyana cewar irin wannan cin zarafi da ake yiwa yan kasuwar su ba yanzu aka fara ba lokuta da dama hallaka musu yayan kungiyar su a jihohin kudancin kasarnan tare da dukiyoyin su wanda har ta sa suka yi yunkurin shiga yajin aiki na kasa Wanda sakamakon hakan gwamnati shigo ciki ta hakurkutar dasu tare da basu tabbacin baiwa yayansu wadanda lamarin ya rutsa dasu diyya Wanda har zuwa yanzu basu ga ko sisin kobo daga wajen gwamnati ba.
Ya kuma kara da cewar daga bisani da suka ga gwamnati ta gaza cika musu alkawarin da ta yi musu shine Shugabancin kungiyar tare da masu ruwa da tsaki suka zagaya jihohin kudancin kasarnan da suke Kai dabbobi suka zauna da gwamnatocinsu aka kulla yarjejeniyar zaman lafiya da juna tare da baiwa yan kungiyarsu tabbacin kare musu rayukansu da dukiyoyin su.
Alhaji Mustafa Ali Ya bayyana cewar yana da yakinin yayan kungiyarsu a shirye suke su zauna lafiya da alummomin da suka tsinci kansu a ciki musamman ma kudancin kasarnan don su gudanar da kasuwacinsu cikin kwanciyar hankali,
Don haka ya san abin da ya faru a jihar Abiya ba wani abu bane Illa kabilanci tsagwaransa.
Don haka Shugaban yayi kira ga gwamnatin tarayya kan ta yi duk maiyiwuwa wajen ganin ta Samawa yayan kungiyar su kariya ta hanyar daukar matakin daya kamata tare da tabbatar da ganin cewar an biya su diyya tare kuma hukunta masu hannu a lamarin ko a wane mataki na gwamnati suke.
Mustafa Ali yace muddin gwamnati ta gaza cika musu alkawarin da ta yi musu ko ta gagara daukar matakin kariya ga yayan kungiyarsu to tabbas ba makawa Zasu daina kai kayayyakin su jihohin kudancin kasarnan har sai sun tabbata gwamnati ta tsayar da magana daya.
Daga karshe Shugaban kungiyar na kasa ya jajantawa yayan kungiyarsu wadanda lamarin ya rutsa da su inda ya basu hakuri tare da basu tabbacin cewar Shugabancin kungiyar a shirye yake wajen yin duk maiyiwuwa don kwato musu hakkokinsu ako ina a fadin kasarnan.