Da yammacin wanna nan rana ta talata aka samu labarin rasuwar fitaccen jarumin fina-finan Hausa, Malam Umar Yahaya Malumfashi.
Marigayin ya kasance fitaccen jarumi da ya taka rawa a fina-finan Hausa da dama ciki har da shirin nan mai dogon zango da ake haskawa a gidan Talabijin na Arewa24, Kwana Casa’in.
Ko a makon jiya sai da aka yi masa hasashen mutuwa wanda daga bisani ya fito ya karyata, kana ya nemi a taya shi da addu’a.