Dan takarar shugaban kasa na jam’iyar NNPP ya fadi abubuwan da zai bawa muhimmanci idan ya zama shugaban kasa

Zan Sake Fasalin Najeriya Tare Habaka Tattalin Arzikin Kasar, Kwankwaso

  Sanata Rabiu Kwakwaso ya fara bayyana abubuwan da zai yi idan ya zama shugaban kasar Najeriya Hukumar zabe ta INEC ta bude filin fara yakin neman zabe tun ranar Larabar da ta gabata Rabiu Musa

Kwankwaso dai shine ɗan takarar da Jam’iyyar NNPP ta tsayar a Shugaban Ĉ˜asa

ĈŠan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Kwankwaso, a ranar Litinin din nan data gabata, ya yi alkawarin habaka tattalin arzikin kasar tare da sake fasalin Nijeriya idan aka mara masa baya a zaben shekarar 2023

Kwankwason ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a Jalingo Babban birnin Jihar Taraba, ya kuma yi alkawarin sanya ilimi a matsayin farko a gwamnatinsa, rahoton Punch.

Tsohon gwamnan jihar Kanon ya kara da cewa gwamnatinsa za ta samar da yanayi mai kyau ga kananan ‘yan kasuwa ta hanyar bunkasa yanayin kasuwancinsu tare da karfafawa mata da matasa gwuiwa dan damawa dasu aharkokin kasuwanci.

Ya kara da cewa, “Za mu ba da fifiko kan ilimi, zamu magance matsalar rashin tsaro da yanayi mai kyau dan haɓaka kasuwanci”

Da wadannan matakan zamu samawar da Ĉ´an kasa damarmaki haɗi da bude musu hanyoyin bunkasa tattalin arzikinsu.

“Za mu inganta abubuwan da ake samarwa a gida da kuma tsarin shigo da kayayyaki da samar da ayyukan yi A cikin gida. Wadannan da ma wasu da dama su ne batutuwan da zamu maida hanakali a kai.

“Kullum muna tashi mu ga Ĉ™udin kasar nan darajarar sa tayi Ĉ™asa, kullum Ĉ™udin kasashen waje kara hawa yak e. wannan na cikin abun da gwanati ta kamata ta kalla; amma ina, ku duba kuga yadda kullum tattalin arziki ke tabarbarewa”

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments