Zan Sake Fasalin Najeriya Tare Habaka Tattalin Arzikin Kasar, Kwankwaso
Sanata Rabiu Kwakwaso ya fara bayyana abubuwan da zai yi idan ya zama shugaban kasar Najeriya Hukumar zabe ta INEC ta bude filin fara yakin neman zabe tun ranar Larabar da ta gabata Rabiu Musa
Kwankwaso dai shine ɗan takarar da Jam’iyyar NNPP ta tsayar a Shugaban Ƙasa
Ɗan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Kwankwaso, a ranar Litinin din nan data gabata, ya yi alkawarin habaka tattalin arzikin kasar tare da sake fasalin Nijeriya idan aka mara masa baya a zaben shekarar 2023
Kwankwason ya bayyana hakan ne lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a Jalingo Babban birnin Jihar Taraba, ya kuma yi alkawarin sanya ilimi a matsayin farko a gwamnatinsa, rahoton Punch.
Tsohon gwamnan jihar Kanon ya kara da cewa gwamnatinsa za ta samar da yanayi mai kyau ga kananan ‘yan kasuwa ta hanyar bunkasa yanayin kasuwancinsu tare da karfafawa mata da matasa gwuiwa dan damawa dasu aharkokin kasuwanci.
Ya kara da cewa, “Za mu ba da fifiko kan ilimi, zamu magance matsalar rashin tsaro da yanayi mai kyau dan haɓaka kasuwanci”
Da wadannan matakan zamu samawar da ƴan kasa damarmaki haɗi da bude musu hanyoyin bunkasa tattalin arzikinsu.
“Za mu inganta abubuwan da ake samarwa a gida da kuma tsarin shigo da kayayyaki da samar da ayyukan yi A cikin gida. Wadannan da ma wasu da dama su ne batutuwan da zamu maida hanakali a kai.
“Kullum muna tashi mu ga ƙudin kasar nan darajarar sa tayi ƙasa, kullum ƙudin kasashen waje kara hawa yak e. wannan na cikin abun da gwanati ta kamata ta kalla; amma ina, ku duba kuga yadda kullum tattalin arziki ke tabarbarewa”