Atiku ya mika sakon ta’aziya ga Iyalan Oladipo Diya

Tsohon mataimakin shugaban kasa Alh Atiku Abubakar ya mika sakon ta’aziya ga Iyalan Oladipo Diya na rashin da suka yi na babban jami’in soja

An Sami labarin rashin ne a sanarwa da ɗansa Barrister Oyesinmilola Diya, ya fitar a madadin sauran iyalansa, ya tabbatar da mutuwar tsohon babban jami’in sojin da safiyar ranar Lahadi.

An dai haifi Janar Oladipo Diya a garin Odogbolu na jihar Ogun da ke kudu maso yammacin Najeriya, yana daga cikin dakarun da suka yi yaƙin basasar ƙaasr nan kafin ya zama babban hafsan sojin ƙasar nan a shekarar ta 1993.

Ya kuma riƙe muƙamin mataimakin shugaban majalisar mulkin soji na ƙasa a shakerar 1994.

Atiku yace tarihi bazai manta da wannan Dan tahaliki ba.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments