Amurka ta umarci ma’aikatan difilomasiyyarta su fice daga Abuja

Amurka ta buƙaci wasu daga cikin jami’an diflomasiyyarta da iyalansu su gaggauta ficewa daga Abuja babban birnin Najeriya sakamakon fargabar kai harin ta’addanci a birnin.

Ofishin jakadancin Amurka a ke Abujar ya bai wa Amurkawa shawarar kar su yi balaguro duk da cewa babu cikakken bayani kan ainahin irin hatsarin da za a fuskanta.

A ranar Laraba Amurka ta fitar da gargaɗi irin wannan a kasar Afirka ta Kudu. Sanarwar ta bukaci Amurkawa mazauna yankin Sandton na masu kuɗi a birnin Johannesburg su guji shiga taron jama’a a karshen makon nan.

Shugaban Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya ce abin takaici ne a ce Amurka ba ta tuntube shi ba kafin ɗaukar wannan ma takin.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments