Kwamatin Kungiyar albirru wattaqawa foundation dake unguwar Danmaliki sun gudanar da rabon tallafin kayan abinci da kayan sakawa ga yara marayu a unguwar Danmaliki.
Wakiliyar Aksammedia ta ruwaito cewa Abubuwan da marayun suka rabauta da su na tallafin sun hada da shinkafa ,masara gero, taliya, da kuma atamfofi.
A zantawar mu da shugaban kungiyar alhaji shuaibu Danmaliki yace sun bayar da tallafin ga matune marasa karfi da kuma Marayu Domin a tafi kafada da kafada tsakanin mai shi da marashi musamman a wannan wata mai albarka na Ramadan dan a gudu tare a tsira tare.
Daga karshe mun zanata da wasu daga cikin wadanda suka rabauta da wannan tallafi kuma sun nuna jindadi da godiya ga kunyiyar.