An katse intanet a Sudan

An katse intanet a kasar Sudan a yayin da ake shirin bikin zagayowar cika shekara daya da gudanar juyin mulkin soja.

 

Ana gudanar da zanga-zanga kusan duk mako a kasar tun bayan da Janar Abdel Fattah al-Burhan ya kwace mulki hannun farar hula.

 

An kashe akalla mutum 118 tun da aka soma zanga-zangar a watan Oktoban bara.

 

Masu rajin kare demokradiyya sun yi kira a gudanar da zanga-zanga a manyan birane da garuruwa a kasar.

 

A Khartoum babban birnin kasar masu rajin kare hakkin dan adam na shirin yin maci zuwa fadar shugaban kasar.

 

Tun bayan da aka hambarar da gwamnatin Omar al-Bashir a shekara ta 2019, sojojin sun yi alkawarin mika mulki ga farar amma har yanzu suna ta jan kafa.

 

 

 

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments