Makarantu 614 da Dalibai 38,000 zasu rabauta da tallafin bankin Duniya a jihar Kano

Bankin Duniya zai kashe zambar kudi har Naira Biliyan daya da digo takwas wajan gyaran makarantun sakandire 614 da tallafawa dalibai a jihar Kano.

Bayanin hakan na kunshe ne cikin jawabin mataimakin shugaban gudanar da aikin Alhaji Nasuru Abdullahi, a ziyar da yakai fadar maimartaba sarkin Bichi Alhaji Nasuru Ado Bayaro.

Abdullahi yace a cikin shirin mata 38,000 zasu Sami horo a Fannin sabuwar kimiyar zamani, kuma Kowacce makaranta an tsara mata aikin da zaayi mata da kudin da za a kashe mata.

Kazalika yace Akwai shirin wayar da kan dalibai wanda Shima za a gudanar dashi cikin wannan lokacin.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments