Buhari ya ayyana Salihu Dembos a matsayin shugaban kafar yada labarai ta NTA
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Mista Salihu Dembos a matsayin Babban Daraktan talabijin ta kasa wato NTA.
Sanarwar nadin na kunshe ne cikin jawabin da Ministan yada labarai da aladu Lai Muhammad yayi a Abuja.
Ministan yace an nada Dembos ne bisa chanchantar sa duba da ya kwashe kimanin shekaru 20 yana aiki a gidan talabijin na NTA din.
A tsawon wannan lokaci ya rike Shugabancin tashar ta Lokoja da kuma ta Kano, kafin nadin kuma shine shugaban sashin cinikayya na hukumar