‘Yan Majalisar tarayya sun soki yawan tawagar da Buhari ya diba zuwa taron UNGA77

‘Yan Majalisa sun soki yawan ‘yan tawagar da Buhari ya kai Amurka

Daga walid Hari

Wasu daga cikin ‘yan majalisar dokokin Najeriya sun soki tawagar kusan mutum 100 da Shugaba Muhammadu Buhari ya jagoranta zuwa birnin New York na Amurka domin halartar babban taron Majalisar Dinkin Duniya.

‘Yan majalisar da ke sukar tawagar, sun ce bai kamata a haɗa dandazon jama’a kusan mutum dari ba a wannan lokaci da Najeriya take fama da matsin tattalin arziki.
A taron da ke zamar wa Buharin na karshe a matsayin shugaban kasa.

Shugaban ya yi jawabinsa na ban-kwana a wajen babban taron

Sai dai ‘yan majalisar irin su Sanata Muhammad Sani Musa, na Majalisar Dattawa, ya ce wannan taro ne da ake yi a kowacce shekara kuma kowa ya ga irin ayarin da yake dauka wajen tafiya irin wadannan tarukan tun hawansa mulki.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments