Wuta ta tashi a ofishin WAEC

An shiga zaman dar-dar bayan da gobara ta tashi a ofishin hukumar shirya jarrabawa Afirka ta Yamma, WAEC, da ke Yaba, Jihar Legas, rahoton The Punch.

Ana juyayin akwai mutane da dama a cikin ginin a yayin da wutar ke cigaba da bazuwa.

Gobara Ta Tashi A Ofishin WEAC, Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Makale A Ciki.

A halin yanzu ba a san sanadin tashin wutar ba. Amma, ma’aikatan bada agajin gaggawa sun isa wurin an kuma kashe gobarar.

Majiyoyi sun bayyana cewa karuwar wutar lantarki a wani ofishin hukumar ne ya janyo gobarar. Da farko an fara ganin hayaki a saman ginin a yayin da wutan ke kona wasu ofisoshi.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments