Daga Jamila Sulaiman Aliyu
A yayin mauludin nabiy na mata zallah anyi kira ga iyaye mata dasu dage wajen yiwa mazajensu biyayya domin biyayyarsu ce zata sadasu da manzon Allah S.A.W
Sidiya asma’u Garba rimin auzunawa ce tayi wannan kiran ga matan a yayin mauludin data shirya tace akowace shekara tana tara mata zallah domin tunatar dasu daraja da martabar ma’aiki da irin hidimar da yayiwa al’ummar musulmi har addininmu na musulunci ya karade duniya.
Malamar ta kuma bayyana cewar matukar mata sunaso soyayyarsu ta zama ta gaske ga annabi to babu shakka sai sun kaucewa wasa da sallah musamman lokutan bukukuwa inda da zarar lokacin sallah yayi to su gaggauta barin duk wani abu da suke yi domin gabatar da sallar.
sayyada Rukayya Allah barmu da soyayyar manzo guda daga aminan sidiya Asma’u Garba tace abin alfahari ne garesu mata masu shirya mauludi ta yadda mazajensu suke basu hadinkai ta kuma ja hankalin mata dasu ci gaba da zama na sahun farko a soyayyar manzon tsira mai’aiki saw.
.taron maudulin ya samu halattar manyan mata a harkar nunawa ma,aiki soyayyar kamar sayyada Fatima da kuma sayyada Husaina Tijjani Bala kalarawi da dai sauransu kuma anyiwa mata nasihohi masu ratsa jiki.