Shugabancin kungiyar masu fataucin Shanu da dabbobi ta Kasa,ta bayyana cewa: a shirye take wajen baiwa duk jamiyyar siysar da za ta baiwa ;ya;yan marayun da wandanda suka samu karyar arziki hadin kai,sakamakon cin mutuncinsu da aka yi a lokacin rikice_rikicen da ya afku da yankungiyar dake safarar Shanu zuwa kudancin kasar nan, domin inganta rayuwarsu.
Cov. Ibrahim Sani gama.
Shugaban kungiyar masu fataucin Shanu da dabbobi ta Kasa Alh Mustafa Ali ne ya tabbatar da haka a zantawarsa da kadaura24 a nan jihar Kano dangane da watsi da rashin cika alkawarin da Gwamnatin tarayya ta dauka na biyan yankungiyar Asarar da suka yi a lokuta daban_daban a sassan jihohin kudancin kasar nan.
Alh Mustafa Ali,ya bayyana cewa kungiyar masu fataucin Shanu da dabbobin ta zauna da kungiyar Dattawan Arewa da manyan jigajigan Gwamnatin tarayya tare da hakurtar da kungiyar wajen daukar mataki saboda cin zarafi da kisan gilla da Asarar dukiyoyin da ake yiwa yan Arewa da suke kai Shanu da dabbobi zuwa kudu,Amma, har yanzu Bata sauya zani ba,kuma,babu wani sakamakon da gudunmawar da aka baiwa wadannan alummar.
Shugaban kungiyar yace,irin wannan rashin daukar mataki da Gwamnatin tarayya da ta jihohin basa yi,yana haifar da matsaloli da dama, musamman wajen Samar da rashin cikakken tsaro da kawo rashin jituwa tsakanin kabilun dake zaman lafiya da juna.inda yace,Kofar kungiyar masu fataucin Shanu da dabbobi ta Najeriya ta shirya tsaf wajen baiwa duk wadanda za su kawowa yankungiyar kulawar da ta dace,wajen ganin an kara tallafawa ya,yanta a koina suke a fadin kasar nan.
Haka kuma, ya kara da cewa kungiyar masu fataucin Shanu da dabbobi ta Kasa da ;ya;yanta sun tafka mutukar asara da rasa rayukan yankungiyar wadanda suke da bukatar a biyasu Diyya domin ci gaba da kula da iyalansu da yanuwansu.
Shugaban kungiyar yace,a wani rahoto da kungiyar ta fitar sakamakon yawan cin mutuncin da yankudancin Najeriya suke yi musu ya nuna cewa sun yi Asarar dukiya sama da miliyan 4000,ban da Asarar rayuka tun Daga farkon Gwamnatin nan zuwa yanzu,kuma,babu wani taimako da aka kawawa kungiyar masu fataucin Shanun a matsayin rage mata radadin zafin cin zarafin da aka yi mata,kamar jihohin Anambra da onatsha,Baylesa da IMO da Dai sauran jihohin da yankungiyar suke shigar da Shanu da dabbobi.
Shugaban kungiyar yayi kira ga shugabannin Arewa da masu Ruwa da tsaki da mahukuntan Arewacin Najeriya da su kasancewa masu kishin yanuwansu,musamman wajen ganin sun karbo musu hakkokinsu domin samun cikakken tsaro da zaman lafiya dauwamamme,kasancewar Gwamnatin tana fafutukar wanzar da zaman lafiya.
Yace,amma rashin cikakken kulawa ga irin wadannan matsaloli na Daga cikin abubuwan da suke kawo koma baya ta fannin harkokin tsaro da kasuwancinsu da farfado da tattalin arziki.
Yace,Dattawan Arewa suna da rawar takawa a irin wannan lokacin da za su, yiwa shugabannin da abin ya Shafa magana ta hanyar da ta dace,shi ya sa suka nemi zama da su tun a lokutan baya domin lalubo bakin zaren matsalolin da suke afkuwa don kaucewa gudun tashin fitina, Wanda yin rigima ba abin da zai haifar sai koma baya a cikin fadin kasar nan.
A don haka kungiyar masu fataucin Shanun ta Kasa tace, tana da alumma da dama a sassan jihohin Najeriya daban daban, kuma,duk Dantakarar da ya taimakawa yankungiyar, ko kungiyoyi da masu hannu da marayuda shugabanni to ,tabbas za su bashi gudunmawar da ta kamata domin samun damar taimakawa marayu
da sauran alummar da suka rasa jairinsu saboda rashin kyautawa da takwarorin alummar kudancin kasar nan suka yi wa yankasuwar dake kai Shanu da dabbobi da sauran kayayyakin masarufin amfanin Yau da kullum a matsayin huddar kasuwanci.
Daga karshe Shugaban kungiyar ya kara da cewa Gwamnatin tarayya ya kamata ta tuna lokacin da kungiyar ta zauna tare da Neman hadin kan kungiyar domin Dakatar da aniyarta na tafiya yajin aikin kai Shanu da dabbobi, zuwa kudu da yi mata alkawarin biyanta Diyya bisa Asarar da aka janyo mata,Amma har Yau ba,a kai ga ciki wannan alkawarin ba
.shi ya sa shugabancin kungiyar yake kira ga duk mai bukatar wannan dama kofarsa a bude take,domin inganta jin dadi da walwalar yayanta.
Ya kuma shawarci yankungiyar da su ci gaba da Bata cikakkiyar gudunmawa da hadin kai domin ci gaba da taimaka musu da kare duk hakkokinsu kodayaushe, musamman wajen Samar da tsaro da bunkasar tattalin arziki da Samar da ayyukan yi ga Matasa domin kaucewa yawan shan muggun kwayoyi da aikata barna a cikin alumma, duba da halin da aka samu kai a ciki na rashin cikakken tsaro a fadin Kasar nan.
/Cov/Ibrahim Sani gama