Yadda al’ummar unguwar Gandun Albasa suka rungumi marayun unguwar su da kyautatawa.
An bukaci Al’ummar sauran unguwanni da garuruwa na jihar Kano da su kafa kungiyoyin kula da marayu da aka rasu aka Bari a yankunan su.
Bukatar hakan ta fito ne daga bakin shugaban kungiyar tallafawa marayu da gajiyaiyu ta Gandun Albasa Malam Lawan Doga Muhammad a zantawar sa da Wakilin AKSAM MEDIA ABDULHAMID ISAH D Z.
Yace idan alumma suna rungumar marayun da aka rasu aka Bari a yankin su to babu shakka alumma zata rayu cikin aminci.
Ya kara da cewa tun a shekarar 2002 suka ga da cewar kafa wannan kungiya kuma kawo yanzu sun tallafawa ‘yaya marayu fiye da 700 a Fannin karatun tun daga firamare da sikandire da kuma zuwa manyan yan makarantun gaba da sikandire.
Da yake tambayar sa yadda suke samun kudaden da suke shida ta marayu da masu karamin karfi
Muhammad yace Akwai iyayen kungiyar da kungiyar take rawa da Bazar su “tun kafa kungiyar Bama fita waje neman taimako komai iyayen kungiyar ne suke wucewa gaba ayi
“Akwai mace guda daya a lokacin kullen Korona cikin sati biyu ta tura kudi fiye da Miliyon bakwai domin a tallafawa marayu da masu karamin karfi.