Tsaro- Wasu matasa sun shiga hannu biyo bayan kamasu da satar waya a kano

Jami’an Hukumar KAROTA sun kama wasu matasa biyu da ake zargin sace wayar Fasinja a cikin Baburin Adaidaita Sahu.

WaÉ—anda ake zargi da satar wayar sun haÉ—a da Ibrahim Sale Rijiyar Lemo da Abubakar Salisu Zoo Road bisa zargin sace wayar fasinjan Adaidaita Sahu Hassan Muhammad Sani

Wanda aka daukewar wayar Hassan Muhammad, ya ce lokacin da ya tsayar da su ya neme su kai shi Bata daga shatale-talen gatar Dangi bayan sun É—auke masa wayarsa sai suka ce ba inda ya bayyana baza su je ba.

Hassan Muhammad, ya kara da cewa bayan da ya sauka ne sai ya fahimci sun É—auke masa, a inda ya nemi taimakon jami’an KAROTA da ke aiki a wannan wuri.

Lokacin da suke hannun Jami’an Karotar matasan sun ce, fiye da shekara guda suna aikata wannan mummunar ta’adar ta É—aukar Fasinja a cikin Baburin Adaidaita Sahu mai lambar KAROTA KRY 1539.

An sami wayoyi iri daban-daban a hannun matasan tare da nau’in kayan shaye-shaye

Shugaban Hukumar ta KAROTA Hon. Baffa Babba ÆŠan’agundi na Æ™ara kira ga al’umma da su cigaba da sa ido a duk lokacin da za su hau Baburin Adaidaita Sahu tare da lura da Koriyar lambar jiki da irin mutanen da suke ciki domin gujewa faÉ—awa hannun É“ata-gari.

Hukumar ta miÆ™a su hannun Rundunar ‘Yansanda ta jihar Kano domin ta faÉ—aÉ—a bincike tare da gurfanar dasu a gaban Shari’a

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments