Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen Jihar zamfara ta ceto mutum 27 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a Ƙaramar Hukumar Anka ta jihar.
Kakakin ‘yan sanda na Zamfara, SP Muhammad Shehu, ya ce an yi garkuwa da mutanen ne a garuruwan Akawa, da Gwashi, da Tungar Rogo da kuma wasu ƙauyuka, inda aka kai su sansanoni a Gando/Bagega da ke dajin Sunka a ƙananan hukumomin Anka da Bukuyum.
Ya ce an yi nasarar ceto mutanen sakamakon rahoton da suka samu cewa ‘yan fashin daji sun kai wa garuruwan hari, amma sai da suka shafe mako ɗaya a hannun maharan.
“Jim kaɗan bayan samun rahoton, Kwamashinan ‘Yan Sanda Kolo Yusuf ya aika da ƙarin ‘yan sanda zuwa ofishinsu na Anka da Bukuyum da kuma ‘yan sa-kai don ceto mutanen,” a cewar sanarwar da SP Shehu ya fitar.
Ya ƙara da cewa 17 daga cikin 27 ne suka isa ofishin ‘yan sandan, yayin da sauran 10 ɗin suke asibiti don karɓar magani.