Daga Khadija Muhammad Maitaya
Babban yaya ga Direban motar da ya yi sanadiyyar faruwa haɗarin da ya yi sanadiyar mutuwar Uwa da danta da suke cikin mahajjatan Jihar Kano Wamban Kabo, Dakta Abdullahi Dahiru Kabo PhD ya mika sakon taaziya ga iyalai da ahlin mamatan.
Dakta Abdullahi Dahiru Wamban Kabo ya miƙa taaziyar ta sa ne a zantawarsa da wakilayayar AKSAMMEDIA, Khadija Muhammad Maitaya inda ya ce ya kadu matuka a lokacin da ya sami labarin faruwar al’amarin
Wamban na Kabo ya bukaci al’umma da su Sanya mamatan a cikin addu’a Allah Subhanahu wata’ala ya karbi shahadarsu yasa aljannatul Firdausi ta zama makoma a gare su.
A karshe ya yi addu’a Allah ya Sanya hakuri da dangana ga daukacin iyalan mamatan tare da addu’a Allah ya sa sauran alhazzai su yi aikin hajji Lafiya









