Barkewar rikici : Gwamnatin Bauchi ta saka dokar hana fita

Gwamnatin jahar Bauchi ta saka dokar hana fita waje na tsawon sa’o’i 24, a karamar hukumar Yelwa, Tsakani, Lushi, Kagadana da kuma Birshi, a sakamakon barkewar rikici a yanki.

Daga Kabiru A. Dukawa

Shugaban ma’aikata na jahar Dacta Aminu Hassan Gamawa ne ya sanar da haka ga manema labarai, inda yace Gwamnati tayi haka ne a kokarin ta na samar da zaman lafiya a yankunan.

Sanarwar tace, an saka dokar ne a sakamakon Wadansu bata gari da suka tada rikici tare da daukar dokar a hannun su wajen fasa shagunan mutane da kone konen Motoci da Gidaje dukiyoyin al’umma da kuma sace sace a yankunan.

Daga karshe Gwamnatin jahar ta gode wa hukumomin tsaro da Sarakunan gargajiya da Malaman addinai da kuma sauran al’umma masu kokarin kiyaye ka’idoji da dokoki da aka sanya a kowanna lokaci a jahar.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments