Tsohon Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Kabiru Ibrahim Gaya, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC) tare da komawa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).
Rahoton SolaceBase ya bayyana cewa, wasikar murabus din mai dauke da kwanan wata 5 ga watan Afrilu, 2026, an aikawa shugaban APC na mazabar Gaya da ke karamar hukumar Gaya a Kano State, inda ya bayyana cewa matakin nasa zai fara aiki nan take.
Sanata Gaya ya ce ya dauki wannan mataki ne bayan “zurfin tunani da kuma tuntubar jama’a da dama,” yana mai jaddada cewa ficewarsa daga APC ya dace da muradun al’ummarsa da kuma akidunsa na kashin kansa.









