Ƙimata za ta zube idan na sake tsayawa takara – Jonathan

Tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya ce ba zai sake tsayawa takarar shugabancin ƙasa ba kasancewar tsayawar za ta zubar masa da ƙima.

A wata tattaunawa da aka yi da shi lokacin bukin ƙaddamar da wani littafi kan rayuwa tsohon limamin cocin fadar shugaban ƙasa, a ranar Talata, Jonathan ya ce ƙaddara ce kawai za ta sanya ya sake zama shugaban Najeriya.

Ya ce amma shi da kansa ba zai taɓa tunanin sake zuwa ya sayi fom sannan ya bi mutane yana roƙon su su zaɓe shi ba.

A baya dai an yi ta raɗe-raɗin cewar tsohon shugaban ƙasar zai sake tsayawa takara a zaɓen  2023.

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
guest
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments